Culture

Masarautar Kaltungo Ta Yi Kira ga Zaman Lafiya Yayin Bukukuwan Eid-el-Kabir

Sagir Usman Saturday, 30 May 2026 30 views

Masarautar Kaltungo ta yi kira ga zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna yayin bukukuwan Eid-el-Kabir. Kiran na kunshe ne a sakonnin da Babban Limamin Kaltungo da Mai Kaltungo suka gabatar a lokacin Sallar Idi da Hawan Sallah.

Al’ummar Musulmi a Masarautar Kaltungo sun gudanar da Sallar Idi ta Eid-el-Kabir tare da bukukuwan Hawan Sallah. Babban Limamin Kaltungo, Liman Muhammad, ya yi kira ga Musulmi su ci gaba da riko da tsoron Allah, ayyukan alheri da taimakon marasa galihu. Mai Kaltungo, Injiniya Saleh Muhammad, ya bukaci al’umma su zauna lafiya tare da karfafa hadin kai tsakanin manoma da makiyaya, sannan ya yi kira ga shugabanni su kara himma wajen samar da abubuwan more rayuwa a karkara. Bukukuwan sun samu halartar masu sarautun gargajiya, kungiyoyin al’adu da dimbin jama’a.


Related News
Residents of Eight Gombe Communities Lament Lack of Basic Amenities, Seek Government Intervention
Read More
Masarautar Kaltungo Ta Yi Kira ga Zaman Lafiya Yayin Bukukuwan Eid-el-Kabir
Read More
Kaltungo Chiefdom Marks Eid-el-Kabir with Prayers, Durbar, and Calls for Peaceful Coexistence
Read More
Cultural Festivals Drive Tourism, Boost Local Economies Across Northeast Nigeria
Read More
BIU EMIR CONFERS JAKADIYAR BIU TITLE ON HAJIYA INNA ADAMU CHIROMA, OTHERS
Read More
ABEDAH Festival Promotes Peace, Culture in Karim-Lamido
Read More